Tambayoyi a Musulunci

ANNABI MUHAMMAD (SAW) BA YA KASHE WANDA YA ZAGE SHI !



Tambaya
Mutane da yawa musamman ‘yan boko akida suna ta tambaya suna cewa: “Babu wani hadisi ingantacce da Annabi SAW ya kashe wanda ya zage shi, hasalima akwai wadanda suka aibata Annabi a gabansa, suka zage shi amma bai kashe su ba, bai Kuma Yi umarni da kashe su ba, don Allah malam Ya abin yake, kuma sahabbai ba su far musu ba” ?

Amsa
Wa alaikum assalam, Allah Yana cewa a cikin suratul Ahzaab aya ta (57): “Tabbas wadanda suke cutar da Allah da mazonsa Allah Ya la’ance su a duniya da lahira Kuma ya tanazar musu da azaba wulakantacciya”

Ka’ab dan Al’ashraf ya kasance Yana cutar da Annabi (SAW), sai Manzon tsira ya shelanta cewa wa zai isar masa game da wannan cutarwar da ake masa?, sai Muhammad dan Maslama Ya ce ya Manzon Allah kana so na kashe shi ? sai ya ce na’am, sai ya tafi gidansa shi da tawagarsa, suka aika shi lahira, bayan ya Yi sabuwar Amarya daga babban gida, Kamar yadda Bukhari ya rawaito a hadisi Mai lamba ta (3811).
Annabi (SAW) ya samu labarin wani Makaho da ya kashe baiwarsa cikin dare, sai ya tambaye shi me yasa ka Yi haka?, sai ya ce ta kasance mai tausasawa gare ni, Kuma Ina da kyawawan Yara da ta haifa mi ni, amma Kuma tana aibanta ka, na kan hana ta, amma sai ta ki hanuwa, jiya da daddare na ji ta tana aibanta ka sai na samo Adda sai na dankara a cikinta, na danna har ta mutu, d’an da yake cikinta ya bulluko, sai Annabi (SAW) ya ce : “Ku shaida tabbas jininta ya ta fi a banza”, Abu dawud ya rawaito shi kuma Albani ya inganta shi a hadisi Mai lamba ta ; (4361).

Ire-iren wadannan hadisan suna da yawa, suna tabbatar da aika duk Wanda ya zagi Annabi (SAW) zuwa Lahira .

Tabbas akwai munafukan da suke aibanta Annabi (SAW) a zamaninsa, suke ci Masa mutunci, Kamar yadda ya zo a suratu Attauba da kuma suratu Almunafikun, amma bai kashe su ba, saboda mutanen da suke gefe za su ce Muhammad Yana kashe sahabbansa, saboda ba za su bambance tsakanin Wanda Ya shiga Musulunci da wasa ba da kuma Wanda ya shiga da gaske, saboda wannan maslahar Annabi (SAW) ya kyale su, don toshe barnar da za ta iya hana wasu shiga Musulunci.

Idan mutum ya ga Arnen da ya zagi Annabi (SAW) bai iya jurewa ba har jami’an tsaro su karaso, ya aika shi Barzahu saboda fusata da kuma sonsa ga manzon tsira, jinin arnen ya tafi a banza, Babu kisasi, mutukar zagin da ya Yi da gangan ne, ba shi da tawili ko shubuhar da ta kasa warwaruwa.
In kuma ya bayyana ba zaginsa ya yi ba, to sai ya biya rabin diyyar Musulmi, amma ba za a kashe shi ba.

Allah ne mafi sani.
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
22/05/2022

See also  HUKUNCIN RATAYA LAYA DA GURU!!!!

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button